Isa ga babban shafi

Jose Peseiro ya kawo karshen horas da Super Eagles ta Najeriya

Jose Peseiro ya bayyana kawo karshen aikinsa na horas da tawagar Najeriya Super Eagles.

Jose Peseiro kenan da yake jinjinawa dan wasan Najeriya Ola Aina, bayan doke Angola da kasar ta yi a gasar AFCON.
Jose Peseiro kenan da yake jinjinawa dan wasan Najeriya Ola Aina, bayan doke Angola da kasar ta yi a gasar AFCON. AP - Sunday Alamba
Talla

Dan kasar Partugal din, ya bayyana hakan ne a cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na X, bayan watanni 22 yana jagorancin kungiyar.

A cewar Peseiro, ya kammala kwantiraginsa da hukumar kwallon kafa ta Najeriya a ranar Alhamis.

Kocin mai shekaru 63, wanda ya karbi ragamar horas da 'yan wasan a watan Yunin 2022 bayan Super Eagles ta kasa samun gurbin shiga gasar cin kofin duniya ta FIFA, ya jagoranci Najeriya zuwa matakin karshe a gasar cin kofin nahiyar Afirka ta 2023 da ta gudana a kasar Ivory Coast, inda Najeriya ta zo na biyu a wasan yayin da Cote D’Ivoire da ta karbi bakunci ta lashe wannan gasa.

A halin da ake ciki kuma, ana danganta Peseiro da komawa horar da ‘yan wasan kasar Aljeriya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.