Fadar Vatican-Turkiyya
Turkiyya ta gayyaci jakadan fadar Vatica kan kisan kiyashi aka yiwa Armeniyawa
Kasar Turkiyya ta gayyaci jakadan fadar Fafaroma ta Vatican dake kasar, domin yayi mata bayani kan manufar kalaman fafaroma Francis dake ikirarin kisan kiyashi aka yiwa Armeniyawa, a hannun dakarun Othman lokacin yakin duniya na farko.Babu dai bayanai gameda abubuwan da ake bukatar sani daga jakadan amma kuma ma’aikatar harkokin wajen Turkiyyan na cewa nan gaba za a fitar da sanarwa kan lamarin.Kasar Turkiyya tasha nuna rashin amincewa da kalaman kisan kiyashi, da aka yiwa Armeniyawa a yakin duniya na farko.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar: