Isa ga babban shafi

Lokaci ya yi da zamu biya diyar cinikin bayi da mukayi - Shugaban Portugal

Shugaban Portugal Marcelo Rebelo de Sousa, ya ce kasarsa ce ke da alhakin aikata laifukan bautarwa da aka yi a lokacin mulkin mallaka, don haka ya ce akwai bukatar a biya diyyar laifukan da aka aikata.

Shugaban Portugal Marcelo Rebelo de Sousa, ya ce kasarsa ce ke da alhakin aikata laifukan bautarwa da aka yi a lokacin mulkin mallaka.
Shugaban Portugal Marcelo Rebelo de Sousa, ya ce kasarsa ce ke da alhakin aikata laifukan bautarwa da aka yi a lokacin mulkin mallaka. © JOSÉ SENA GOULÃO/LUSA
Talla

Akalla ‘yan Afirka miliyan 12 da dubu dari 5 ne aka yi safaransu ta hanyar jiragen ruwa zuwa Turai, inda aka sayar da su a matsayin bayi.

Daga cikin wancan adadi, Portugal kadai ta fitar da ‘yan Afrika miliyan 6 da ta sayar dasu a matsayin bayi, lamarin da ya sanyata zama kasar da ta fi yawan cinikayyar bayi a nahiyar Turai.

A lokacin da shugaba Rebelo de Sousa ke ganawa da manem alabarai a jiya Talata, ya ce kasarsa ce ke da alhakin duk wani lafin bautarwar da aka samu a baya, don haka ya ce lokaci ya yi da ya kamata su biya diyar laifukan da aka aikata.

Ko a shekarar da ta gabata, sai da shugaban na Portugal ya nemi afuwa kan tsarin bautar da suka yi da kuma mulkin mallaka, duk da cewa a jiya Talata ya ce daukar alhakin laifin ne yafi muhimmanci.

Fafutukar da ake yi na ganin an biya diyar laifukan bautarwar da aka yi a baya na samun karbuwa a duniya, ciki kuwa harda kokarin samar da kotu ta musamman da za ta yi shari’a kan lamarin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.