Isa ga babban shafi
Turkiya

An zabi Erdogan a matsayin shugaban kasar Turkiyya

Firai Ministan kasar Turkiyya Recep Tayyip Erdogan ya lashe zaben shugabancin kasar tun a zagayen farko da aka gudanar a ranar lahadin da ta gabata.

Recep Tayyip  Erdogan, zababben shugaban kasar Turkiyya a ranar 10 ga watan Agustan 2014
Recep Tayyip Erdogan, zababben shugaban kasar Turkiyya a ranar 10 ga watan Agustan 2014 REUTERS/Murad Sezer
Talla

Erdogon, ya samu kashi 52% na kuri’un da aka jefa, inda yake shirin soma aiki a cikin makonni biyu masu zuwa. Zababben shugaban kasar dai ya bayyana cewa kasar za ta shiga wani sabon babi na ci gaba bayan da al’umma suka danka amanarsu a hannunsa.

Erdogon ya `zama Firai Minista ne tun a shekara ta 2003, kuma a yanzu zai karbi ragamar shugabancin kasar ne daga hannun Abdullah Gul wanda ya share tsawon shekaru 10 akan wannan matsayi.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.