Ma'aikatan lafiya sama da 4,000 suka bar Ghana zuwa aiki a kasashen Turai
Afirka – Akalla ma’aikatan kula lafiyar kasar Ghana da aka fi sani da nas-nas sama da 4,000 suka gudu daga kasar zuwa kasashen Turai da Amurka domin samun ayyukan da ake biyan albashi mai tsoka a wannan shekara, sabanin abin da ake biyan su a cikin gida, matsalar da ta haifar da karancin ma’aikata a asibitocin da ake da su a fadin kasar.
Wallafawa ranar:
Sakatare Janar na Kungiyar Nas-Nas da Unguwar Zoma a Ghana, Dr David Tenkorang-Twum ya ce tsakanin watan Janairu zuwa Yuli na wannan shekarar ta 2023, kusan nas-nas dubu 10 da 209 suka gabatar da bukatar samun takardar barin kasar saboda samun guraban ayyukan yi a kasashen ketare.
Jami’in ya ce daga cikin wannan adadi, kusan 4,000 sun samu takardar amincewa, kuma yanzu haka suna can inda suke aiki a kasashen waje.
Jami’ar ta bayyana takaici a kan yadda kwararrun ma’aikatan su ke ficewa, yayin da matakin ke budewa wadanda suka rage kofar tafiya.
Ministan Lafiyar Ghana, Kwaku Agyemang Manu ya ce suna aiki tare da kungiyoyi cikin gida da na kasashen waje domin yadda za’a tinkari matsalar.
Manu ya kuma ce suna kuma aiki tare da ma’aikatar kwadago domin yi wa dokar Ghana gyaran fuska ta yadda za a takaita yadda ma’aikatan ke ficewa suna barin gida.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu