Isa ga babban shafi
Faransa

Faransa za ta takaita zirga-zirgar ababen hawa a Paris

Hukumomin kasar Faransa sun sanar da daukar matakin takaita zirga-zirgar ababen hawa domin rage cinkoso a Paris, babban birnin kasar

Gurbatar yanayin da hayaki ya haifar
Gurbatar yanayin da hayaki ya haifar AFP/
Talla

Wannan matakin na zuwa ne, domin rage gurbatar yanayi a faransa, kamar yadda Anne Hidalgo, magajiyar garin Paris ta sanar.

Matakin zai takaita Cunkoson ababan hawa, da zai rage hayakin da su ke fitar wa wanda ke matukar yin illa ga lafiyar al’umma.

Wannan dai, bashi ne karo na farko ba, da hukumomin kasar faransa ke daukar wannan matakin, yayinda a bara, an dau irin wannan matakin, saboda matsanancin sanyi cikin dare,da zafi da rana, dake hana hayakin motoci bajewa, tare da haddasa gurbatar yanayin.

A makon daya gabata, gurbatar yanayi a faransa, ya kai wani mizani daya zarce na biranen New Delhi da Beijing, inda suma ke fama da irin wannan matsalar.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.