Isa ga babban shafi
Macedonia

‘Yan Majalisun Macedonia sun ba hamata iska game da kasafin kudin shekara

An samu sabani a Majalisar Macedonia inda aka bai wa hammata iska tsaknin ‘Yayan jama’iyya mai mulki da ‘Yan adawa, a majalisar dokokin kasar. Rikicin ya barke ne sakamakon muhawarar da ake yi akan kasafin kudin shekara mai zuwa.

Jami'an tsaro suna kokarin raba 'Yan Majalisu fada bayan barkewar rikici a zauren Majalisar Macedonia tsakanin 'Yan adawa da 'Yan Jam'iyya mai mulki game da kasafin kudin.
Jami'an tsaro suna kokarin raba 'Yan Majalisu fada bayan barkewar rikici a zauren Majalisar Macedonia tsakanin 'Yan adawa da 'Yan Jam'iyya mai mulki game da kasafin kudin. REUTERS/Viktor Popovski
Talla

A daya bangaren kuma magoya bayan jama’iyyun da ke adawa da juna sun yi ta jifar junansu da duwatsu da kwalabe a harabar majalisar.

Dubun dubatar masu zanga zanga ne suka nufi majalisar, bayan magoya bayan jama’iyyar adawa ta ‘yan gurguzu, sun killace harabar majalisar, don nuna adawa da shirin amincewa da kasafin kudin, da suka ce zai sa a yi ta kashe kudaden gwamnati ba kakkautawa.

‘Yan Majalisa biyu ne dai suka samu rauni sanadiyyar rikicin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.