Gwamnatin sojan Nijar ta rusa majalisun kananan hukumomin kasar
Gwamnatin mulkin sojan Nijar ta rusa dukan majalisun kananan hukumomi na jiha da manyan birane a fadin kasar tare da maye gurbinsu da kantomomi.
Wallafawa ranar:
A wata sanarwa da shugaban mulkin sojan kasar ya rattabawa hannu da aka karanta da gidan talbijin na kasar ya bayyana cewa an dauki matakin ne bisa kokarin wasu gyare-gyare.
Wadanda aka korar dai yawancinsu zababbu ne a tsohuwar gwamnati da suka share watanni 8 suna jan zarensu, tun bayan hanasu taba kudaden da’irorinsu a makon jiya akayi hasashen korarsu daga mukaman.
Tun a baya dai ‘Yan kungiyoyin fararen hula sun yi ta caccakar sojojin da cewa sun yi juyin mulki amma sun bar magajan gari kan mukamansu abin da ga al'ada ba a taba gani ba.
A ranar 26 ga watan Yulin shekarar 2023 ne sojojin suka kifar da gwamnatin dimokaradiyyar kasar, karkashin jagorancin shugaba Bazoum Muhammane.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu