Sojin Najeriya sun kashe Boko Haram 300
Ma’aikatar Tsaron Najeriya tace ta yi nasarar kashe mayakan Boko Haram sama da 300 tare da kwace garuruwa 11 da ke hannun Mayakan a Jihar Borno bayan kaddamar da yaki akansu a cikin mako guda.
Wallafawa ranar:
Mai Magana da yawun ma’aikatar tsaron kasar Manjo Janar Chris Olukolade ya sanar da haka inda ya ke cewa sun kwace tarin makamai daga hannun kungiyar.
Jami’in ya ce Mayakan sun kashe sojoji biyu yayin da wasu 10 suka samu raunuka.
Sojojin Najeriya sun karbe ikon garuruwan Mongono da Marte da ke cikin Jihar Borno da Mayakan Boko Haram suka kwace a ranar 25 ga watan Janairu.
A cikin wata sanarwa, Janar Olukolade ya ce sun kuma karbe wasu kauyuka da ke yankin.
Boko Haram dai ta kwace garuruwa da dama a Jihohin Borno da Yobe, tare da kashe dubban mutane a yankin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu