Isa ga babban shafi
Boko Haram

Za mu dagula zabe a Najeriya- inji Shekau

Shugaban Mayakan Boko Haram Abubakar shekau ya sha alwashin dagula zaben da za a gudanar a Najeriya a cikin wani sakon bidiyo da ya aiko a Twitter a ranar Talata bayan wasu munanan hare haren kunar bakin wake da mayakan shi suka kai a garin Biu inda mutane 38 suka mutu.

Abubakar Shekau, jagoran kungiyar Boko Haram
Abubakar Shekau, jagoran kungiyar Boko Haram YouTube
Talla

Shekau ya ce ko za su mutu za su dagula zabe a Najeriya wanda za a gudanar a ranar 28 ga watan Maris.

Wannan ne karon farko da kungiyar ta aiko da bidiyo a Twitter, a wani sabon salon na canza yadda kungiyar ke yada sakwanninta bayan nadar sakwannin baya a DVD.

A cikin bidiyon Shekau ya ce su suka kai harin Gombe.

Boko Haram dai na ci gaba da zama barazana a Najeriya bayan dage zaben kasar bayan Jami’an tsaro sun ce suna bukatar lokaci domin kawo karshe kungiyar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.