Za mu dagula zabe a Najeriya- inji Shekau
Shugaban Mayakan Boko Haram Abubakar shekau ya sha alwashin dagula zaben da za a gudanar a Najeriya a cikin wani sakon bidiyo da ya aiko a Twitter a ranar Talata bayan wasu munanan hare haren kunar bakin wake da mayakan shi suka kai a garin Biu inda mutane 38 suka mutu.
Wallafawa ranar:
Shekau ya ce ko za su mutu za su dagula zabe a Najeriya wanda za a gudanar a ranar 28 ga watan Maris.
Wannan ne karon farko da kungiyar ta aiko da bidiyo a Twitter, a wani sabon salon na canza yadda kungiyar ke yada sakwanninta bayan nadar sakwannin baya a DVD.
A cikin bidiyon Shekau ya ce su suka kai harin Gombe.
Boko Haram dai na ci gaba da zama barazana a Najeriya bayan dage zaben kasar bayan Jami’an tsaro sun ce suna bukatar lokaci domin kawo karshe kungiyar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu