Mazauna Michika sun nemi samun kariya daga Boko Haram
Mazauna garin Michika da ke Jihar Adamawa a tarayyar Najeriya sun bukaci taimakon gwamnatin kasar saboda abin da suka kira yunkurin Boko Haram na kwace garinsu.
Wallafawa ranar:
Wannan na zuwa ne bayan hare haren da ‘yayan kungiyar suka kai garuruwan Gulak da Michika a karshen mako.
Majiyoyi sun ce dimbin magoya bayan kungiyar dauke da makamai sun afka wa garin ne tun a karshen makon da ya gabata, lamarin da ya sa jama’a suka rika tsere suna barin garin.
Haka zalika wasu rahotanni sun tabbatar da cewa sojojin gwamnati sun samu nasarar kwace garin Bama daga hannun ‘yan kungiyar ta Boko Haram.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu