Boko Haram ta kai hari a Gulak da Minchika
Rahotanni daga Najeriya na tabbatar da cewa mutanen garuruwan Gulak da Minchika a Jihar Adamawa da dama ne ke tserewa zuwa Yola da Mubi da wasu wurare daban daban bayan da Mayakan Boko Haram suka abka wa garuruwan. Rahotanni daga Gulak sun ce tun da sanyin safiya ne aka yi musayar wuta tsakanin ‘Yan Boko Haram da Sojojin Najeriya, amma daga baya ‘yan Boko Haram suka fi karfin Sojin na Najeriya, lamarin da ya sa suka tsere zuwa garin Shuwa.
Wallafawa ranar:
Zuwa yanzu dai babu tabbaci ko Mayakan na Boko Haram sun karbe ikon Gulak bayan sun karbe Madagali a Jihar Adamawa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu