CAF za ta dauki mataki akan mutuwar Ebosse a fili
Shugaban hukumar kwallon Afrika Issa Hayatou ya yi Allah waddai da jifar Dan wasan Kamaru Albert Ebosse da aka yi a cikin fili a kasar Algeria wanda ya yi sanadin mutuwarsa. Wani daga cikin ‘Yan kallo ne ya jefi dan wasan, kuma ya mutu ne bayan an garzaya da shi zuwa Asibiti.
Wallafawa ranar:
Dan wasan na Kamaru shi ne ya fara jefawa kungiyar shi JS Kabylie kwallo a raga amma abokiyar hamayya USM Alger ita ce ta lashe wasan ci 2-1.
Shugaban Hukumar kwallon Afirka Issa Hayatou yace ba zasu amince aika-aika ba daga yan tayar da tsaune tsaye, don haka dole su dauki mataki akai
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu