Burundi
Hukumomin Burundi sun bayar da umarnin kawo karshen zanga zangar kasar
Gwamnatin kasar Burundi ta umarci masu zanga zangar kasar su gaggauta kawo karshen boren da suka shafe makonni da suna yi, don nuna adawa da yunkurin Pierre Nkurunziza ke yi, na ci gaba da rike madafun ikon kasar karo na 3. Kwamin tsaron kasar ta Burundi, da shugaba Nkurunziza ke jagoranta, ya umarci masu zanga zanga sun janye shigayen da suka sa a kan titunan kasar.Kwamtin yace zanga zangar, da shingayen da aka sun durkusar da harkokin yau da kulum a kasar, don haka a cewar hukumomin, dole a kawo karshen su.
Wallafawa ranar: