Isa ga babban shafi

An soma taron kolin kasashen musulmi na OIC karo na 15 a birnin Banjul

Shugabanni da dama daga kasashen musulmi sun fara isa birnin Banjul na kasar Gambia inda ake soma taron kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC karo na 15,taron da zai tattauna batutuwa da dama har da rikicin Hamas da Isra’ila.

Harabar Masallacin Birnin Kudus na uku mafi daraja ga Musulman duniya.
Harabar Masallacin Birnin Kudus na uku mafi daraja ga Musulman duniya. Reuters
Talla

Rahotanni daga Banjul na bayyana cewa,kusan kasashe 57 ne suka aika da wakili a taron da za a soma ranar Lahadi sai dai ,tsirarun shugabannin kasashen Afirka ne suka yi wannan balaguron, kamar na Senegal.

Babban sakataren kungiyar Hissein Brahim Taha a yayin bude taron ya na mai cewa "wannan taro na Banjul ya zo ne a cikin yanayi mai tsanani da ba a taba ganin irinsa ba a cikin al'ummar Falasdinu, Isra’ila na ci gaba da kisan fararren hula a idanun manyan kasashen Duniya.

Wasu masu ibada a masallaci
Wasu masu ibada a masallaci © AFP

Hissein Brahim Taha ya yi kira ga kasashen kungiyar OIC da su “kara kaimi da hadin kai wajen tabbatar da al’ummar Falasdinu”, tare da bayyana cewa dole ne a dauki matakin musamman kan Falasdinu a karshen taron a ranar Lahadi.

Wasu daga cikin masu zanga-zanga a jami'o'in Amurka
Wasu daga cikin masu zanga-zanga a jami'o'in Amurka AP - Susan Walsh

A watan Nuwamban shekarar 2023, kungiyar ta gana a birnin Riyadh don gudanar da wani taron hadin gwiwa da kungiyar hadin kan kasashen Larabawa, inda ta yi Allah wadai da matakin da sojojin Isra'ila suka dauka a Gaza, amma ta kaurace wa sanar da daukar matakan ladabtarwa na tattalin arziki da siyasa kan Isra'ila.

Tutocin kasashen Africa
Tutocin kasashen Africa AFP - MICHELE SPATARI

Wannan taron dai ya nuna rarrabuwar kawuna a yankin dangane da yadda za a mayar da martani ga rikicin, dangane da fargabar barkewar rikici a yankin.

A ranar Asabar ne dai hankali ya fi karkata kan kasar Masar, inda wata tawaga daga Gaza ta isa don tattaunawa kan shirin tsagaita wuta a Gaza.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.