Isa ga babban shafi
Kungiyar Tarayyar Turai

Taron Afirka kan cutar Ebola a birnin Addis Ababa

Hukumar gudanarwa ta Kungiyar Tarayyar Afirka na gudanar da taro a wannan litinin domin samar da karin dubaru na yaki da cutar Ebola da ke ci gaba da kashe jama’a a yankin yammacin nahiyar.

Aikin fada da cutar Ebola a Liberia
Aikin fada da cutar Ebola a Liberia Reuters TV/Files
Talla

Taron wanda ke gudana a birnin Addis Ababa, na samun halartar wasu kwararri kan sha’anin kiwon lafiya daga kasashe daban daban na nahiyar, yayin da wasu tawagogi daga kasashen yammacin Afirka da ke fama da cutar za su yi wa taron karin bayani kan halin da ake ciki a yankin.

Kawo yanzu dai an tabbatar da mutuwar mutane fiye da 2000 sakamakon kamuwa da cutar a kasashen Liberia, Sierra Leone, Guinea Conakry da kuma Najeriya.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.