Isa ga babban shafi
Ebola

AU ta kira taron gaggawa kan Ebola

Kungiyar Kasashen Afrika ta AU ta kira taron gaggawa a makon gobe don tattaunawa kan matsalar cutar Ebola da ta shafi kasashe biyar a Yammacin Afrika. Kungiyar tace taron da za’a yi a ranar litinin zai duba matsalar cutar da kuma dakatar da sufurin jiragen sama da jiragen ruwa da rufe iyakokin wasu kasashe da kyamar da ake nunawa mutanen da suka fito kasashen da ke fama da cutar Ebola.

Ana gwajin Kwayar Cutar Ebola da ke kisa cikin hanzari a yammacin Afrika
Ana gwajin Kwayar Cutar Ebola da ke kisa cikin hanzari a yammacin Afrika facebook.com/WHO
Talla

Hukumar Lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya tace adadin mutanen da suka mutu sakamakon kamuwa da cutar Ebola sun haura 1,900 yanzu haka, inda ta gargadi kasashen da aka samu cutar da su dauki kwararan matakai.

Shugabar Hukumar Margareth Chan tace a cikin wanna makon an gano cewar adadin wadanda suka kamu da cutar a Guinea da Saliyo da Liberia sun kai 3,500, kuma 1,900 sun mutu.

Tace adadin ya tashi daga 1,552 da aka sanar sun mutu a makwannin da suka gabata.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.