Isa ga babban shafi
Burundi

Burundi na barazanar murkushe masu zanga-zanga

Gwamnatin Kasar Burundi ta yi barazanar amfani da sojoji don murkushe masu zanga zangar adawa da shirin shugaban kasar Pierre Nkurunziza na neman wa’adi na uku sabanin yadda kundin tsarin mulkin kasar ya tanada. Ministan tsaron kasar Janar Pontien Gaciyubenge, ya ce aikin sojojin ne su tabbatar da tsaro kuma duk lokacin da shugaban kasa ya ba su umurni za su aiwatar.

Jami'an tsaro na murkushe masu zanga-zanga a Burundi
Jami'an tsaro na murkushe masu zanga-zanga a Burundi REUTERS/Jean Pierre Aime Harerimana
Talla

A ranar juma’ar da ta gabata an yi taho mu gama tsakanin ‘Yan Sanda da masu zanga zangar da suka fito daga Jam’iyyu 6 na kasar inda aka kama mutane 65 daga cikinsu tare da tuhumarsu da laifin yin tawaye.

A watan Juni al’ummar kasar Burundi za su jefa kuri’ar zaben shugaban kasa inda ‘yan adawa da kungiyoyin fararen hula ke kokarin haramtawa shugaban kasar mai ci yin tazarce.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.