Isa ga babban shafi
Burundi

An yi arangama tsakanin ‘Yan sandan Burundi da mabiya darikar Katolika

Akalla mutane shida ne suka rasa rayukansu a wata arangama da ‘Yan sandan kasar Burundi suka yi da wata kungiyar mabiya Darikar Katolika da ke karrama wata mata da ake kira Zebiya.

'Yan sandan kasar Burundi suna arangama da masu zanga-zanga
'Yan sandan kasar Burundi suna arangama da masu zanga-zanga AFP PHOTO/Esdras NDIKUMANA
Talla

Rikicin ya barke ne da sanyin safiya inda daruruwan mabiya kungiyar wata mata da ake kira Zebiya wadanda ‘Yan asalin darikar katolika suka yi arangama da ‘Yan sandan kasar Burundi, a yayin da suke kokarin isa kan wani tsauni da suka mayar wajen kai ziyara domin girmama matar.

Akalla mutane shida ne suka mutu a cewar Gwamnan yankin Kayanza, inda anan ne lamarin ya faru, wasu mutane 35 daban suka samu raunuka.

Kodayake ‘Yan sanda hudu sun samu munanan raunuka, a arangamar, sai dai Gwamnan yankin na Kayanza, Athanase Mbonabuca ya ce dukkanin wadanda suka mutu daga bangaren mabiya kungiyar ta Zebiya ne a yayin da a yanzu haka wasu daruruwa ke hannu.

Rahotanni na nuna cewa dangantaka tsakanin ‘Yan kungiyar ta Zebiya da Mujam’iar Katolika a ‘yan watanni nan na kara tabarbarewa.

A watan Disambar bara ne ‘Yan sanda suka tarwatsa wani gini da ‘Yan kungiyar suka yi a kan tsauni da suka mayar da shi wajen ibada.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.