An samu barkewar cutar Typhoid a jihar Kaduna sakamakon damuna
Wallafawa ranar:
Kunna - 10:19
Shirin Lafiya Jari ce tare da Azima Bashir Aminu a wannan mako ya yi duba kan tsanantar cutar Typhoid a jihar Kaduna ta arewacin Najeriya, wanda masana ke alakantawa da gurbatar ruwan da jama'a ke ta'ammali da shi yayin hada-hadar yau da kullum.
A cikin shirin na wannan mako za ku ji hirarraki da kwararru a bangaren abincin kan yadda mutane za su inganta ruwan da suka amfani da shi da nufin kaucewa wannan cuta mai matukar hadari, sai kuma jawabin likitoci kan matakan kula da kai bayan kamuwa da cutar da ma yadda za a bi don samun waraka.
Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakken shirin.........
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu