Isa ga babban shafi
Venezuela

Venezuela : Maduro ya kira taron gaggawa na kudancin Amurka

Shugaban kasar Venezuela Nicolas Maduro ya bukaci kasashen yankin Kudancin Amurka da su kira taron gaggauwa domin tattauna rikicin siyasar da ake fama da shi a kasar.

Shugaban kasar Venezuela, Nicolas Maduro
Shugaban kasar Venezuela, Nicolas Maduro ©REUTERS/Jorge Silva
Talla

Kiran na shugaban Maduro na zuwa ne kwana daya bayan da ya kori jakadan kasar Panama da ke birnin Caracas, bayan da gwamnatin Panaman wadda ke da alaka ta kut da kut ta yi kira ga kasashen yankin su gudanar da wani taro domin daukar mataki akan gwamnatin kasar ta Venezuela mai fama fa tarzomar ‘yan adawa.

‘Yan adawa a kasar ta Venezuela suna nuna rashin gamsuwarsu ne akan irin kamun ludayin Maduro game da mulkin kasar wacce ke da arzikin man fetur bayan ya gaji Marigayi Hugo Chavez.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.