Isa ga babban shafi
Libya

‘Yan bindiga sun sake kaddamar da hari a Libya

Rahotanni daga kasar Libya sun ce ‘Yan bindiga sun sake kaddamar da sabbin hare hare a tashar jiragen saman birnin Tripoli kwanaki biyu bayan yunkurin tattaunawar zaman lafiya ya ci tura. Wani jami’in tashar jiragen saman Al Jilani Al Dahesh yace an kai hare haren na yau ne da rokoki da bama bamai da kuma tankin yaki.

Hayaki ya turmuke sama a tashar jirin sama a birnin Tripoli na Libya
Hayaki ya turmuke sama a tashar jirin sama a birnin Tripoli na Libya REUTERS/Hani Amara
Talla

Ko a ranar juma’a, Libya ta bukaci taimakon Majalisar Dinkin Duniya wajen kare tashoshin jiragen sama da kuma rijiyoyin mai.

Rahotanni sun ce mutum guda ya rasa ransa a fadan tsakanin mayakan Zintan da ke gwagwarmaya tare da wasu mayaka don kafa gwamnati.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.