Isa ga babban shafi
Najeriya

Wasu Mutanen Damboa sun yi hadarin mota

Rahotanni daga Jihar Barno sun ce wasu 'yan gudun hijira daga Damboa da ke neman tsira da rayukansu sakamakon hare haren Boko Haram sun samu hadarin mota, inda yawancinsu suka jikkata. Kwamishinan yada labaran jihar Dr Muhammad Bulama ya tabbatar da faruwar hadarin

Wani harin Bom da Mayakan Boko Haram suka kai a Jahar Borno a Najeriya
Wani harin Bom da Mayakan Boko Haram suka kai a Jahar Borno a Najeriya AFP PHOTO/STRINGER
Talla

Kwamishinan yace mutanen sun samu hadarin ne, a lokacin da suna gudun hijira akan hanyarsu zuwa Biu saboda halin kuncin da suka shiga a Damboa sakamakon munanan hare haren da Mayakan Boko Haram suka kai.

Mutane da dama ne dai aka ruwaito sun mutu a Damboa a jiya Juma’a bayan Mayakan Boko Haram sun bi gida gida suna jefa bama bamai tare da bude wa fararen hula wuta.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.