Isa ga babban shafi
Kenya

‘Yan bindiga sun kashe mutane da dama a Kenya

Akalla mutane 29 aka tabbatar da mutuwarsu a wasu hare hare da ‘Yan bindiga suka kai a wasu yankuna gudana biyu a kasar Kenya, kamar yadda mahukuntan kasar suka tabbatar. ‘Yan sanda sun zargi wasu ‘Yan a ware a kasar duk da Mayakan Al Shabaab na Somalia sun yi ikirarin daukar alhakin kai hare haren.

Mutanen Kauyen Hindi a yankin Lamu inda aka kai hare hare a kasar Kenya
Mutanen Kauyen Hindi a yankin Lamu inda aka kai hare hare a kasar Kenya REUTERS/Athman Sheikhuna
Talla

Ma’aikatar cikin gida tace mutane Tara aka kashe a harin da aka kai a yankin Lamu a ranar Assabar, kusa da inda aka taba kashe mutane sama da 60 a wani hari da aka kai a watan jiya.

Mutane 20 ne kuma aka kashe a wani hari da aka kai a ofishin ‘Yan sanda a Gamba da ke yankin Tana River County.

‘Yan sanda sun zargi kungiyar ‘Yan a ware ta Mombasa Republican Council, amma kungiyar Al Shabab tace ita ce ta kai hare haren.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.