Isa ga babban shafi
Hague

Kwamandan ‘Yan tawayen Uganda ya isa kurkukun ICC

Kwamandan ‘Yan tawayen Lord’s Resistance Army na Uganda ya isa kurkugun kotun hukunta manyan laifukan yaki ta ICC a birnin Hague domin fuskantar shari’ar zargin  laifukan yaki da cin zarafin Bil adama da ya aikata a kasashen da ke tsakiyar Afrika. Kakakin Kotun Fadi El Abdallah ya shaidawa Kamfanin dillacin labaran Faransa cewa sun karbi dominic Ongwen a birnin Hague wanda ya mika kansa ga dakarun Amurka a Jamhuriyar tsakiyar Afrika.

Hoton Kwamandan 'Yan yawayen Uganda Dominic Ongwen a wata jaridar kasar.
Hoton Kwamandan 'Yan yawayen Uganda Dominic Ongwen a wata jaridar kasar. AFP PHOTO / ISAAC KASAMANI
Talla

Ongwen yana cikin shugaban ‘Yan yawayen Uganda wadanda ake zargi da kisan mutane sama da 100,00 a ta’adin da suka fara a 1987.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.