Isa ga babban shafi
Turkiya

Ma’aikatan kwadago sun shiga yajin aiki a Turkiya

Babbar kungiyar Kwadago a kasar Turkiya ta kira yajin aikin kwana guda sakamakon mutuwar ma’aikatan hako Ma’adinai kusan 300 da suka mutu a cikin kasa. Kungiyar ta kira shiga yajin aikin ne domin juyayin mutuwar ma’aikatan da kuma kira ga gwamnatin kasar ta inganta aikin hako ma’adinai.

'Yan sanda suna arangama da masu zanga-zangar adawa da gwamnati bayan samun mutuwar daruruwan ma'aikata hako ma'aidinai
'Yan sanda suna arangama da masu zanga-zangar adawa da gwamnati bayan samun mutuwar daruruwan ma'aikata hako ma'aidinai REUTERS/Cevahir Bugu
Talla

A yau Alhamis ne aka fara zaman makoki a kasar Turkiya sakamakon mummunan al’amarin da ya faru da ma’aikatan a garin Soma.

Akwai kuma yanzu daruruwan ma’aikatan da suka makale a cikin kasa, yayin da ake ci gaba da aikin ceto su.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.