China/Sin
Murar tsuntsaye mai tsanani na bazuwa cikin kasar China
Jami’an kiyon lafiyar yankin Jiangsu da ke gabashin kasar Sin a yau talata, sun ce an samu karin wasu mutane 4 da suka kamu da cutar murar tsuntsaye nau’in H7N9.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Talla
Kwayar cutar da a karon farko a cikin ‘yan kwanakin nan bayyana ga dan adam a birnin Shangai, wadda kuma ta yi sanadiyar mutuwar mutane 2.
An gano kwayar cutar ne dai, ga wasu Mata 3 ‘yan shekaru 45-48 da kuma 32, da kuma wani namji dan shekaru 83 a duniya, dukkaninsu kuma na rayuwa ne a wasu garuruwa 4 da ke yankin da ke makwabtaka da birnin na Shanghai.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu