Isa ga babban shafi
Ecuador

Gwamnatin Ecuador za ta yi bayani akan mafakar Assange

Shugaban kasar Ecuador Rafael Correa yace a cikin wannan makon ne, ya ke sa ran nazarin bukatar wanda ya kirkiro shafin kwarmato na Wikileaks, Julian Assange ta neman mafaka a kasar bayan ya nemi mafaka a ofishin jekadancin kasar a London.

Shugaban Shafin kwarmata bayanan Siri na WikiLeaks,  Julian Assange.
Shugaban Shafin kwarmata bayanan Siri na WikiLeaks, Julian Assange. Reuters/Finbarr O'Reilly/Files
Talla

Assange, mai shekaru 41 da haihuwa, ya sami mafakar siyasa a ofishin jakadancin kasar ta Ecuador da ke birnin London, tun a ranar 19 ga watan Yuni, don kaucewa mika shi kasar Sweden, inda ake zargin shi da laifin yin fyade.

Assange yace yana fargabar idan aka mika shi Sweden, daga can kuma za a iya mika shi Amurka, don a tuhumar shi da laifin leken asiri.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.