Isa ga babban shafi
Syria

‘Yan tawayen Syria sun karbe Jisr al Shughur

‘Yan tawayen Syria sun karbe ikon garin Jisr Al-Shughur, gari na karshe da ke hannun ikon gwamnatin kasar a lardin Idlib. Rahotanni sun ce dakarun Gwamnati sun yanka fursunoni 23 da suka kame kafin su fita garin na Jisr.

'Yan tawayen Syria a cikin garin Jisr al Shughur da suka kwace a lardin Idlib
'Yan tawayen Syria a cikin garin Jisr al Shughur da suka kwace a lardin Idlib REUTERS/Ammar Abdullah
Talla

Tun a ranar Alhamis ne ‘yan tawayen na Syria tare da taimakon mayakan Al Qaeda suka kaddamar da farmaki a yankin, kuma rahotanni sun ce har zuwa yau Assabar suna ci gaba da gwabza fada da dakarun gwamnatin Syria.

Masu sa ido a rikicin kasar sun ce dakarun shugaba Bashar Assad sun fice daga yankin bayan ‘Yan tawaye sun fatattake su.

Rahotanni sun ce akalla mutane 10 aka kashe a musayar wutar da aka yi tsakanin ‘Yan tawaye da dakarun gwamnati.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.