SYRIA
Mayakan ISIL dubu 2 ne suka mutu a Syria-Rahoto
Wata kungiyar kare hakkin dan Adam da ke kasar Syria tace a kalla mayakan IS dubu 2 ne suka mutu, sakamkon hare-haren da Amurka ke jagoranta a kasar Syria.
Wallafawa ranar:
Talla
A wani rahaton da Kungiyar ta fitar, tace akasarin mutane da suka mutu a hare haren da aka shafe watanni 7 da aka shafe ana wa mayakan na IS luguden wuta ta sama ‘yan kasashen waje ne.
Kungiyar ta kuma ce Gamayyar kasashen duniya suna ci gaba da far wa maboyar mayakan na IS a tsakiyar birnin Homs da Alppo a rewacin kasar, sai kuma Hasakeh arewa maso gabashi, da Deir Ezzor a gabashi.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu