Dakarun Syria sun karbe ikon wasu yankunan Damascus daga hannun ‘Yan tawaye
Dakarun Gwamnatin Bashar Assad sun fatattaki rundunar ‘Yan Tawaye daga wasu yankunan birnin Damascus, mako guda bayan ‘Yan Tawayen sun kaddamar da yaki a babban birnin kasar. yanzu haka ana ci gaba da gwabza yaki a hedikwatar Jami’an tsaro a birnin Aleppo.
Wallafawa ranar:
‘Yan rajin tabbatar da Demokradiya masu adawa da Gwamnatin Assad sun tabbatar da karbe ikon yankin Mezzah a Damascus tare da bayyana cewa dakarun Gwamnati sun kashe farin kaya mutane 20 da suke zargin sun taimakawa ‘Yan Tawaye.
Dakarun Gwamnati sun kaddamar da yaki ne domin daukar fansar kisan wasu manyan Jami’an gwamnatin Assad da ‘Yan tawaye suka kashe a wani harin Bom da aka kai a ranar Larabar makon jiya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu