Isa ga babban shafi
Burundi

Burundi ta yi watsi da zargin bude wuta ga masu zanga zanga

Gwamnatin kasar Burundi ta yi watsi da zargin da ake mata na cewa jami’an tsaro sun budewa masu zanga zanga wuta a wani fito na fito da ‘yan sanda kan matakin sake tsayawa takarar Shugabancni kasar na Shugaba Pierre Nkuruziza  

Jami'an tsaron Kasar Burundi
Jami'an tsaron Kasar Burundi Photo : RFI / SR
Talla

Ministan cikin gidan kasar ta Burundi Gabriel Nizigama ya shaidawa taron manema labarai cewa, a hukumance,  jami’an tsaro a za su yi aiki da doka domin dakile duk wata zanga zanga da za a gudanar ba bisa ka’ida ba.

Nizigama ya kara da cewa, kawo yanzu bai samu bayani ba na cewar jami’an tsaro sun yi amfani da makamai domin tarwatsa ma su zanga zanga.

Ya kuma jaddada matsayin Burundi wajan kula da doka, inda ya siffanta ta da kasa mai aiki da doka da oda, kuma ya ja hanklulan al-umma cewa a horon da aka baiwa jami’an tsaron babu ta yadda za su bada goyan baya a tarzomar da za ta kai ga kashe fararen hula.

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.