Wani soja a kasar Burundi ya rasa ransa a tarzomar kin amincewa da tazarcen shugaban kasar kan mulki
Wani sojan kasar Burundi ya rasa ransa a cigaba da tarzoma da mutan kasar ke yi saboda yunkurin shugaban kasar na neman zarcewa kan karagar mulkin kasar a zani sabon wa’adi na uku a jere.
Wallafawa ranar:
Bayanai na nuna ceza harbe sojan aka yi, yayin da wasu mutanen 9 suka sami raunuka awannan boren da ake ci gaba da gudanarwa a birnin Bujumbura babban birnin kasar.
Majiyoyi dai sun bayyana cewa wani jamiin tsaro ne ya yi harbin bisa kuskure ya kuma dirke abokinsa har lahira.
Kawo yanzu dai yawan wadanda suka rasa rayukansu a cikin zannan tarzoma dai sun kai mutane goma
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu