Isa ga babban shafi
Kamaru-Boko Haram

Boko Haram ta kashe mutane 10 a kamaru

Majiyoyin tsaro a kasar Kamaru sun ce mayakan Boko Haram sun kai hari a wasu garuruwa da ke yankin Kolofata da ke gab da iyakar da Najeriya inda suka kashe mutane akalla 10.

Shugaban kungiyar Boko Haram, Abubakar Shekau.
Shugaban kungiyar Boko Haram, Abubakar Shekau.
Talla

Rahotanin sunce, Maharan sun tsallaka kan iyaka zuwa cikin Najeriya, kafin sojojin Kamaru su iso.

Harin dai na zuwa ne a daidai lokacin da sojojin kasar da kuma na Chadi ke ci gaba da farautar mayakan kungiyar ta Boko Haram a yankin.

Kungiyar Boko Haram ta sha kai hare-hare a arewacin Kamaru da Chadi da kuma Nijar, amma mafi yawancin hare-harenta a Najeriya ne.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.