Isa ga babban shafi
Yemen

'Yan tawayen Yemen na kokarin shiga Mafakar Shugaban Kasar

Akalla Mutane 30 sun mutu a wata musayar wuta tsakanin Dakarun Gwamnatin Kasar Yemen da ‘Yan tawayen da ke kokarin kutsa kai domin shiga birnin Aden, inda Shugaban Kasar Abdul-Rabuh Mansur Hadi ke da mafaka  

Mayakan Huthis na Yemen
Mayakan Huthis na Yemen REUTERS/Khaled Abdullah
Talla

A bangare guda, bayan karbe ikon filin jirgin sama dake birnin Taez da sansanin soji mai nisan kilimiter 180 da ke arewacin birnin Aden, ‘Yan tawayen sunyi ajalin wasu mutane 5 wadanda ke zanga-zangar adawa da ayyukansu

Mayakan sun yi nasarar karbe ikon wurare da dama a kasar Yemen, amma a yanzu birnin Aden suke fako, inda shugaba Hadi ya tsere bayan daurin talala da ga hannun mayakan.

Masana dai na ganin cewa, idan har mayakan suka yi nasarar karbe ikon Aden, to hakika kasar zata fada cikin rikicin da zai zama matsala ga sauran kasashen duniya

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.