Isa ga babban shafi

Tiani ya yi alkawarin gabatar da jawadalin mika mulki ga farar hula

Jagoran gwamnatin sojojin da suka yi juyin mulki a Jamhuriyar Nijar, ya ce a cikin wannan mako, zai bayyana wa al’ummar kasar jadawali dangane da yadda za a gudanar da zabuka da kuma mika mulki ga fararar hula.

Shugaban mulkin sojin Nijar Janar Abdourahmane Chiani. 16/09/23
Shugaban mulkin sojin Nijar Janar Abdourahmane Chiani. 16/09/23 © Presidence du Niger
Talla

Janar Abdourahman Tiani, wanda ya  bayyana haka yayin gabatar da jawabi a game da zagayowar ranar Jamhuriya, ya yi amfani da kakkausan harshe wajen sukar matakan da kungiyar Ecowas ta dauka kan Nijar, yayin da a hannu daya ya bayyana alfahari da matakin da suka dauka na soke wasu yarjejeniyoyi da ke tsakanin Nijar da Faransa.

01:02

Jawabin shugaban gwamnatin sojin Jamhuriyar Nijar Janar Abdourahamane Tiani

A ranar Juma'ar da ta gabata kungiyar kasashen yammacin Afrika ta ECOWAS ta amince da cewar an yi juyin mulki a Jamhuriyar Nijar, bayan tabbatar da hakan a hukumance ne kuma, ECOWAS din ta dakatar da kasar daga cikinta har sai lokacin da aka mayar da kundin tsarin mulki.

Takunkuman da ECOWAS ta kakaba wa Jamhuriyar Nijar dai na ci gaba da yin tasiri a bangarori da dama, musamman akan harkokin kasuwanci inda dubban 'yan kasuwa a ciki da  makwaftan kasar suka tafka hasarar kayayyakinsu da suka makale akan iyaka, sakamakon matakin ladaftarwar da hukumomin kasa da kasa suka dauka kan sojojin da suka yi juyin mulki.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.