Isa ga babban shafi

Rasha na shirin tattauna batun soke yarjejeniyar hana gwajin makamin Nukiliya

Kasar Rasha na shirin tattauna batun soke amincewa da yarjejeniyar hana gwajin makamin Nukiliya, kamar yadda kakakin majalisar dokokin kasar ya fada a yau Juma’a. Vyacheslav Volodin ya bayyana hakan ne kwana guda bayan da shugaban kasar Vladimir Putin ya bayyana yiwuwar daukar wannan mataki, wanda zai iya kara dagula al'amura a tsakanin Rasha da kasashen Yamma.

Shugaban kasar Rasha Vladmir Poutine
Shugaban kasar Rasha Vladmir Poutine AP - Sergey Guneyev
Talla

Wannan al’amari na Rasha na zuwa ne  a daidai lokacin da Moscow ke kaddamar da hare-haren soji a Ukraine.

Rasha a taron majalisar kasar na Duma za a  tattauna batun soke amincewa da yarjejeniyar hana gwajin makaman nukiliya," in ji Volodin a cikin wata sanarwa.

Shugaba Rasha Vladmir Poutine
Shugaba Rasha Vladmir Poutine © 路透社图片

Hakan zai zama martani ga Amurka wacce har yanzu ba ta amince da yarjejeniyar ba da kuma ke bayar da taimako ga kasar Ukraine a wannan yaki da Rasha.

A shekara ta 2000 ne Rasha ta amince da yarjejeniyar. Washington ta ba da sanarwar dakatar da gwaje-gwaje a cikin 1992 kuma a cikin 1996 ta sanya hannu kan yarjejeniyar haramcin gwajin amma har yanzu ba ta amince da ita ba.

Wani yankin kasar Ukraine da Rasha ta kai hari
Wani yankin kasar Ukraine da Rasha ta kai hari via REUTERS - KHARKIV REGIONAL PROSECUTOR'S OF

Rasha daga Shugaban kasar Putin,‘‘yana yiwuwa a soke amincewa, kuma idan muka yi hakan, zai wadatar."

Shugaban na Rash ana fadar hakan ne a wani taron kungiyar Tattaunawa ta Valdai a jiya Alhamis.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.