Isa ga babban shafi
Yemen

Shugaba Hadi ya tsere daga birnin Aden

Rahotannin daga kasar yemen na cewa Shugaba Abedrabbo Mansur Hadi ya gudu daga birnin Aden inda yake mafaka, a kokarin sa na tserewa mayakan Huthi, da a yanzu haka ke dab da isa fadar gwamnatin Aden

Yan tawayen Yémen
Yan tawayen Yémen REUTERS/Anees Mahyoub
Talla

Fada na ci gaba da tsananta a kasar ta yemen, inda a yanzu yan tawayen huthi sun karbe ikon sansani soji dake kusa da fadar gwamntin Mansur Hadi a kudanci Aden, kwanaki kalilan bayan kasar Amurka ta janye dakarun ta daga yankin

Wasu rahotanin sunce Shugaba Hadi yayi amfani da jirgi mai sauka angula ta fadar Al-Maasheeq wajen ficewa daga birnin Aden

Yanzu dai sansani sojin Al-Anad na karkashin iko mayakan Huthi bayan wata musayar wuta da taimakon yan tawayen kasar masu goyon bayan tsohon shugaba Abdallah Saleh da kuma dakarun gwamnati Hadi

Tuni dai kasar saudiya ta aike da dakarunta iyakar kasar ta da Yemen domin kare kasar ta daga barazanar tsaro
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.