Isa ga babban shafi
Yemen

Mansur Hadi Ya sake neman bukatar haddin kai MDD akan rikicin kasar Yemen

Shugaban Kasar Yemen Abdurrabu Mansur Hadi ya sake bukatar kwamitin sulhu na majalisar Dinkin Duniya da ya amince da wani sabon kudiri da zai hana fadada hare haren mayakan Houthi dake neman kama garin Aden inda ya samu mafaka

Shugaban kasar Yemen, Abdrabuh Mansur Hadi.
Shugaban kasar Yemen, Abdrabuh Mansur Hadi. REUTERS/Stringer
Talla

A wasikar da ya aikewa Jakadan Faransa dake shugabancin kwamitin, Hadi ya bayyana fargabar cewar kungiyar Al Qaeda na iya anfani da halin da ake ciki wajen lalata al’amura a cikin kasar.

Ya kuma bukaci majalisar da ta karbe makamai masu linzamin da yanzu haka yan tawayen suka kwace daga rumbun ajiyar gwamnati.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.