Isa ga babban shafi
Saudi

Saudiya ta bulale wanda ya ci zarafin Musulunci

Gwamnatin kasar Saudiya ta fara zartar da hukuncin bulala 1,000 a bainar Jama’a ga mutumin da ya ci zarafin addinin Islama a Intanet. A yau Juma’a an yi wa Raef Badawi bulala 50 kafin makwanni masu zuwa ya kammala shan sauran bulalar.

via dailymail
Talla

Kotu ta kuma yanke ma sa hukuncin daurin shekaru 10 a gidan yari.

Amurka da kungiyar kare hakkin Bil’adama ta Amnesty International sun bayyana adawa da hukuncin.

An zartar wa Badawi hukuncin ne bayan kammala Sallar Juma’a a Masallacisn Al Jafali a birnin Jedda a bainar Jama’a.

Saudiya kuma ta ci tarar Badawi kudi Riyal Miliyan guda tare da haramta ayyukan kungiyarsa da ke yada manufofin cin mutuncin Musulunci a shafin Intanet.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.