Shehin Malamin Saudiya ya soki Mayakan IS na Iraqi
Alkalin alkalan kasar Saudi ya yi Allah waddai da da ayyukan Mayakan IS da suka ayyana sabuwar daular Islama bayan sun mamaye wani yanki na Iraqi da Syria. Shehin Malamin ya danganta Mayakan a matsayin manyan makiyan addinin musulunci. Sheikh Abdul Aziz al-Sheikh yace, tawaye da ta’addanci ba koyarwan musulmi ba ne.
Wallafawa ranar:
Malam Nuru Khalid malammin addini, kuma shugaban kungiyar kira, da binciken harkokin addinin Musulunci a Najeriya yace tun tuni ya kamata Saudiya ta yi Allah waddai da ayyukan Mayakan.
Malam Nuru Khalid yace akwai bukatar Matasa su nemi karin ilimi domin kaucewa abkawa ayyukan ta’adanci.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu