Iraq
An kashe 'yan Yazidi akalla 80 a arewacin Iraki
Hukumomin yankin Kurdistan mai cin gashin kansa daga kasar Iraki, sun ce mayakan Daular Islamiyya sun kashe ‘yan kabilar Yazidi akalla 80 a wani kauye da suka kai wa hari.
Wallafawa ranar:
Talla
Wani dan majalisar dokoki da ke wakilar yankin da lamarin ya faru Hoshiyar Zebari, ya bayyana cewa mayakan sun shiga garin ne inda suka tattara jama’a a wuri daya, inda suka kashe 80 daga cikinsu sannan suka awun gaba da wasu mata.
Yanzu haka dai MDD ta sanar da soma bincike domin tantance wadanda ke taimaka wa mayakan.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu