Isa ga babban shafi
Malaysia-Australia

Malaysia: An dakatar da neman jirgi saboda matsalar yanayi

A karo na biyu cikin mako guda, an dakatar da neman jirgin kasar Malaysia na wuccin gadi wanda ya bata dauke da Fasinja 239 kusan makwanni uku, saboda matsalar kyawon yanayi a yankin tekun India, inda ake kyautata zaton jirgin ya fadi.

Jiragen sama da ke aikin neman jirgin Malaysia da ya bata.
Jiragen sama da ke aikin neman jirgin Malaysia da ya bata. REUTERS/Rob Griffith/Pool
Talla

A cewar hukumar da ke kula da ayyukan ruwan kasar Australia da ke jagorancin neman jirgin, ba a ganin yankin tekun na India da kyau saboda rashin kyawun yanayin.

Jiragen kasashe da dama ne suke aikin neman jirgin na Malaysia, kuma wasu hutunan da Faransa ta hango a tauraron dan adam an ga wasu abubuwa masu yawa da ke kama da tarkacen jirgi a cikin tekun India.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.