Isra’ila ta yi watsi da rahotan da ke cewa guba ce ta kashe Arafat
Shugaban Kasar Isra’ila, Shimon Peres, ya yi watsi da rahotan binciken da ya nuna cewar guba aka sanyawa tsohon shugaban Falasdinawa, Yaseer Arafat, a matsayin abinda ya hallaka shi.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Peres ya ce bai gamsu da rahotan ba, domin idan ana bukatar kashe Arafat, da harsashi kawai za’ayi amfani da shi a saukake.
A kwanan ne wani bincike da aka gudanar a kasar Switzerland ya bayyana cewa guba aka sanyawa Arafat ya mutu lamarin da ya janyo cecekuce a duniya.
Lamarin har ila yau ya sa shugaban Falasdinawa Mahmud Abbas ya nemi da a gudanar da kasashen duniya su gudanar da bincike mai zaman kansa domin a gano wake da hanu wajen kashe Arafat.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu