Isa ga babban shafi
Isra'ila

Isra’ila ta yi watsi da rahotan da ke cewa guba ce ta kashe Arafat

Shugaban Kasar Isra’ila, Shimon Peres, ya yi watsi da rahotan binciken da ya nuna cewar guba aka sanyawa tsohon shugaban Falasdinawa, Yaseer Arafat, a matsayin abinda ya hallaka shi.

Shugaban Isra'ila, Shimon Peres
Shugaban Isra'ila, Shimon Peres REUTERS/Peter Dejong/Pool
Talla

Peres ya ce bai gamsu da rahotan ba, domin idan ana bukatar kashe Arafat, da harsashi kawai za’ayi amfani da shi a saukake.

A kwanan ne wani bincike da aka gudanar a kasar Switzerland ya bayyana cewa guba aka sanyawa Arafat ya mutu lamarin da ya janyo cecekuce a duniya.

Lamarin har ila yau ya sa shugaban Falasdinawa Mahmud Abbas ya nemi da a gudanar da kasashen duniya su gudanar da bincike mai zaman kansa domin a gano wake da hanu wajen kashe Arafat.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.