Sojojin Najeriya sun kai hari dajin sambisa
Rahotannin sun ce, Sojojin Najeriya sun kai hari a dajin Sambisa, wurin da ake gani a matsayin maboya kungiyar Boko Haram ta karshe. Kakakin rundunar sojin, Chris Olukolade, ya sanar da cewar sojin suna kai farmaki a dajin Sambisa, wanda ke kusa da kan iyakar Najeriya da Kamaru.
Wallafawa ranar:
Gwamnatin Najeriya dai ta sha alwashin dakile hare-haren Mayakan da’a yanzu suka kai shekara 6 suna tada zaune tsaye
A baya dai Shugaba Najeriya mai barin gado Goodluck Jonathan ya sha alwashin kawo karshan kungiyar, kafin rantsar da shugaba mai jiran gado, Janar Muhammadu Buhari, a ranar 29 ga watan Mayu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu