Isa ga babban shafi
Nijar-Canada

Boko Haram: An Umurci Sojojin Canada su fice Diffa

Ma’aikatar tsaron Canada ta umurci dakarunta na musamman da ke ba Sojojin Nijar horo akan su fice daga yankin Diffa da ke kusa da kan iyaka da Najeriya saboda barazanar Boko Haram. Sai a watan Maris ne Sojojin za su kammala aikin amma Ma’aikatar tsaro ta bayyana fargaba akan Mayakan Boko Haram na iya abkawa Sojojin.

Dakarun Nijar da ke fada da Boko Haram na Najeriya
Dakarun Nijar da ke fada da Boko Haram na Najeriya RFI/ Nicolas Champeaux
Talla

Sojin na Canada suna cikin rundunar sojin kasashe 19 na hadin guiwa karkashin jagorancin Amurka da ke aikin bayar da horo ga sojojin kasashen Afrika guda biyar.

Ma’aikatar tsaron tace an rarraba Sojojin zuwa Agadez da Yamai a Nijar da kuma garin N’Djamena na Chadi a cikin wani sakon Email da ta aikawa kamfanin Dillacin Labaran Faransa,

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.