Isa ga babban shafi
Afrika ta Tsakiya

Dakarun Faransa sun yi gumurzu da ‘Yan Seleka

An yi wani kazamin dauki ba dadi tsakanin dakarun kasar Faransa da tsoffin mayakan yan tawayen kungiyar Saleka a garin Batangafo, da ke yankin arewacin kasar Jamhuriyar Afrika ta tsakiya, inda rahotani suka bayyana cewa ‘yan tawaye da dama sun rasa rayukansu a cikin fadan.

Mayakan Seleka a kasar Jamhuriyyar Afrika ta tsakiya
Mayakan Seleka a kasar Jamhuriyyar Afrika ta tsakiya REUTERS/Goran Tomasevic
Talla

Wani Sojan rundunar tsaro da Afrika MISCA ya shaidawa kamfanin dillacin labaran Faransa cewa dakarun Faransa sun budewa ‘Yan tawayen Seleka wuta bayan sun abkawa garin Batangafo a ranar Litinin.

Sojan yace ‘Yan tawayen Seleka da dama ne aka kashe a musayar wuta da suka yi da dakarun Faransa.

Hedikwatar dakarun kasar Faransa a birnin Paris ta tabbatar da wannan gumurzu, tare da cewa ‘yan tsageran kungiyar Saleka cike a budaddiyar mota wasu kuma a kan babura suka abkawa dakarun Fransar da manyan makaman yaki.

Faransa dai tace babu ko sojanta da ya rasa ransa ko rauni a harin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.