Isa ga babban shafi
Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya

Kungiyar Seleka ta bukaci a raba Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya

Wakilai fiye da 200 daga bangarori daban daban da ke da hannun a rikicin Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya ne ke halartar taron sulhu wanda aka buda ranar litinin ta wannan mako a birnin Brazaville na kasar Congo.

Shugaba Samba-Panza-nguesso
Shugaba Samba-Panza-nguesso
Talla

Taron wanda ke gudana a karkashin jagorancin shugaban kasar ta Congo Denis Sasso Nguesso, na samun halartar shugabar rikon kwarya ta Afirka ta Tsakiya Catherine Samba-Panza, da wakilai ‘yan tawayen Seleka da kuma na sauran jam’iyyun siyasa.

Jagoran tawagar ‘yan tawayen Seleka a taron Mohamed Moussa Dhaffane, a cikin wata sanarwa da ya karanta a gaban mahalarta taron, ya bayyana cewa babban bukatarsu ita ce raba kasar domin samun dawwamammen zaman lafiya.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.