Isa ga babban shafi
Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya

Sabon fada a birnin Bangui na Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya

Sabon rikici ya barke a birnin Bangui na Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya a daidai lokacin da ministan tsaron Faransa Jean-Yves Le Drian ke soma ziyarar aiki a kasar.

Sojojin kasa da kasa a birnin Bangui
Sojojin kasa da kasa a birnin Bangui AFP PHOTO/MARCO LONGARI
Talla

Rahotanni sun ce fada ya barke ne tsakanin magoya bayan kungiyar Seleka da kuma Anti-balaka gab da lokacin da ministan ya isa kasar, inda aka tabbatar da mutuwar akalla mutum daya tare da raunata wasu a kusa da wata mujami’a da ke birnin.

Wannan ne dai karo na bakwai da ministan na Faransa ke kai ziyarar aiki a kasar mai fama da rikicin addini da kabilanci, inda jim kadan bayan isarsa a birnin Bangui Le Drian ya ziyarci barikin sojan Mpoko wanda shi ne babban sansanin da daruruwan sojojin Faransa ke amfani da shi a matsayinsu na masu aikin wanzar da tsaro da zaman lafiya a kasar.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.