Isa ga babban shafi
Burkina Faso

Kotun Burkina ta ki bayar da umurnin a tono gawar Sankara

Babbar Kotun kasar Burkin Faso ta yanke hukuncin cewa ba ta da hurumin yanke wata kara da aka shigar gabanta da ke neman a sake tono gawar tsohon Shugaban kasar na soja Thomas Sankara.

Tsohon Shugaban Burkina Faso Thomas Sankara
Tsohon Shugaban Burkina Faso Thomas Sankara William F. Campbell/Time & Life Pictures/Getty Images
Talla

Matakin kotun ya harzuka dangi da ‘yan uwan tsohon Shugaban wanda aka kashe a juyin mulkin da aka gudanar a 1987 da ya kai ga shugaba mai ci yanzu Blaise Campore hawa kujeran Mulki.

A wancan lokaci marigayi Thomas Sankara da wasu manyan sojoji 14 aka kashe tare da yin gaggawar binne su ba tare ‘yan uwa da dangin sun yi tozali da gawawwakinsu.

A shekara ta 2010 ne dangi da ‘yan uwan mamatan suka nemi kotu ta bayar da izini a tono gawarsu domin a gudanar da bincike.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.